Wq/ha/Balaraba Ramat Yakubu

From Wikimedia Incubator
< Wq‎ | ha
Wq > ha > Balaraba Ramat Yakubu

Balaraba Ramat Yakubu kwarariyar marubuciyar littafan Hausa ne da ake wa lakabi littattafan soyayya. An haife ta a cikin birnin Kano a a shekarar 1959[1] . Tana daga kalilan marubuta da aka fassara littafinta zuwa harshen Turanci. Rubuce - rubucenta sun fi bada muhimmanci akan zamantakewar aure da kuma gwagwarmayar mata a rayuwar Hausawa, musamman tauye hakkin mata da mazan Hausawa kan yi, zamu ga haka a littattafan ta kamar Budurwar zuciya da mashahurin littafin ta Alhaki kuikuyo ne.

Azanci[edit | edit source]

  • Talla masifa ce ga mata.
    • [1] Balaraba ta zanta haka a hirar ta da jaridar Aminiya.
  • Mu musulmai ne kuma muna da dokokin addinin mu na Musulunci a kan sha'anin aure. Amma a wasu lokuta al'adun mu suna maye gurbin addinin kuma al'adu da addini ba ɗaya bane. Ina yaki saboda ina so na nuna cewa addini da al'adu ba na da bambanci.
  • We are Muslims and we have rules in Islam for marriage and so on. But sometimes, our culture dominates the religious dictates and culture and religion are different. So, I fight because I want to stress that culture and religion are different. Probably that is why I'm called a controversial writer.
  • ...Ina taɓa maudu'in da wasu marubuta suke tsoron yin rubutu a kan su. A baya, wasu dattawa kamar tsararrakin mahaifiyata suna tunanin cewa mijin su shine na biyu bayan Ubangijin su amma sai na wayar da su cewa mijin su kamar tsaran su ne.

Manazarta[edit | edit source]

  1. Femke van Zeijl, "From illiterate child bride to famous Nigerian novelist", Al Jazeera (Features), 8 March 2016.