Wq/ha/Aisha Dikko
Appearance
Aisha Dikko, Ita ce lauya janar kuma Kwamishiniyar Shari’a ta yanzu a Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Kaduna. An rantsar da ita a matsayin lauya janar kuma Kwamishiniyar Shari’a ta Jihar Kaduna a ranar 12 ga watan Yuli, 2019 a lokacin mulkin Nasir Ahmad el-Rufai.
Zantuka
[edit | edit source]- Don haka, mun ga dacewar mu kawo lauyoyin nan domin sabunta tunaninsu kan yadda za su gabatar da shaidu na Na'ura a cikin shari’unsu. Muna son inganta kwarewarsu domin su gabatar da mafi kyau a kotu.
- Zan iya cewa fyaɗe ya zama kamar annoba a cikin al’umarmu da kuma faɗin ƙasa baki ɗaya, kuma abin takaici, akwai wata alama ta tozarci da ake ɗora wa waɗanda aka yi wa fyaɗen. Saboda wannan dalili, ba laifi ba ne da mutane da yawa ke iya yarda da cewa ya faru da su. Amma game da fyaɗe, idan mutum ya yi shiru, wanda ya aikata laifin zai ci gaba da aikatawa ba tare da wani kalubale ko shinge ba. Abin da nake ƙoƙarin cewa a wajen taron shi ne, eh, lallai fyaɗe wani abu ne na kunya musamman a cikin al’ummarmu, amma mutane suna buƙatar su fara kai rahoton waɗanda ke aikata fyaɗe da laifukan fyaɗen domin hakan zai taimaka sosai wajen rage yawan aikata irin waɗannan laifuka. Wani abu kuma da muka lura da shi shi ne, ana sa wa waɗanda abin ya shafa da iyalansu matsin lamba su rufe batun, kuma hakan yana da mummunan tasiri ga al’umma. Don haka, mutane su riƙa kai rahoton irin waɗannan laifuka domin masu laifi su sami hukunci. Idan sun san za a gurfanar da su kuma a yanke musu hukunci saboda fyaɗe, hakan zai zama gargaɗi ga waɗanda ke tunanin aikata irin wannan laifi.
- Commissioner Aisha Dikko spoke about Rape Daily trust
- Hukuncin da aka yanke da kuma umarnin da aka samu akan Gwamnatin Tarayya ba su da wani tasiri akan Gwamnatin Jihar Kaduna, wadda ba ta kasance ɓangare a cikin waɗancan shari’o’i ba, kuma ba'a yanke wani hukunci a kanta ba. Duk wani batu da ya shafi bin umarnin kotu ko rashin bin sa da DSS ko Gwamnatin Tarayya suka yi, ba za'a iya amfani da shi a matsayin hujja don rushe shari’ar da Gwamnatin Jihar Kaduna ta fara akan El-Zakzaky ba.
- An rungumi tsarin sarrafa shari’u a Ma’aikatar domin inganta bayar da service da kuma sauƙaƙa ware shari’u yadda ya dace domin adanawa cikin tsari. Ma’aikatar ta horar da lauyoyi ta hanyar jerin horo daban-daban, domin samar musu da ƙwarewar da za ta basu damar yin aiki a kowane lokaci daga kowanne wuri.
- Na san cewa, da gwamnatin tarayya ta ba da isasshen lokaci mai ma'ana kafin aiwatar da tsarin sauya fasalin naira, duk wannan wahala da hasarar da jihohin masu kara da kuma jama'ar jihohi ke fuskanta da za'a iya guje musu. Na san cewa ƙarin kwanaki 10 da gwamnatin tarayya ta bayar bai isa ba domin magance matsalolin da ke tattare da wannan tsari. Haka kuma, na fahimci cewa gwamnati ba ta da hurumin hana 'yan Najeriya canza tsoffin takardun kuɗinsu a kowane lokaci, ko da kuwa takardun ba su sake zama doka ba.
- Aisha Dikko talked about Old naira currency Business Day
- Gwamnatin da ke zuwa kotu a matsayin madaidaicin wurin warware shari’o’i ba za'a iya zarginta da rashin girmama doka da oda ba cikin adalci. Waɗanda ke da'awar akasin haka na da alhakin bayyana yadda za'a inganta bin doka ba tare da amfani da kotuna ba, kuma ko al’umma za ta fi cin gajiyar barin mutane su yi abin da suka ga dama, ko rikice-rikicen da ke rikita fahimtar 'yancin faɗar albarkacin baki.
- Aisha Dikko gave verdict as the Minister of justice Premium times
- A kokarin dawo da kwarewar aikin koyarwa da kuma inganta matsayin ilimi a makarantun fadin jihar, an gudanar da jarabawar kwarewa ga malaman makarantun firamare na gwamnati a jihar, a ranar 3 ga watan Yuni, shekarar 2017.
- Aisha Dikko as the judge between Nut and El-Rufai The Cable'Vanguard